Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sakatare Janar na MDD ya jajantawa iyalan wadanda gobarar Beirut ya rutsa da su
2020-08-05 10:01:42        cri
Sakatare Janar na MDD Antonio Guterres, ya aike da sakon jaje ga iyalan wadanda gobarar Beirut ta rutsa da su.

Wata sanarwa da kakakin sa Farhan Haq ya fitar, ta ruwaito Antonio Guterres na jajantawa iyalai da al'umma da gwamnatin Lebanon, biyo bayan fashewar wani abu a birnin na Beirut a jiya. Inda ya yi wa wadanda suka jikkata fatan samun sauki, ciki har da jami'an majalisar dake aiki a Lebanon.

Ya kara da cewa, MDD za ta ci gaba da ba Lebanon goyon baya a wannan muhimmin lokaci, kuma tana taimakawa wajen shawo kan lamarin.

Wasu abubuwa biyu da suka fashe sun girgiza birnin na Beirut a jiya Talata, lamarin da haddasa mutuwar mutane 50 tare da jikkata wasu 2,500.

Gobarar ta auku a tashar ruwa ta Beirut da misalin karfe 6:10 na yamma agogon kasar, inda ta girgiza gine-gine a fadin birnin da jikkata mutane tare da lalata abubuwa da dama. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China