Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Morocco ta tsawaita matakin ta-baci a bangaren lafiya da wata 1 domin yaki da COVID-19
2020-07-10 10:24:02        cri
Kasar Morocco ta tsawaita matakin ta baci kan bangaren kiwon lafiya da ta sanya tun ranar 24 ga watan Maris, da wata 1 domin yaki da annobar COVID-19.

Yayin wani taron manema labarai, kakakin gwamnatin kasar, Saaid Amzazi, ya ce matakin da aka ayyana a fadin kasar, zai tsawaita har zuwa 10 ga watan Augusta, a matsayin wani bangare na yaki da annobar COVID-19.

Morocco ta bada rahoton samun sabbin mutane 308 da suka kamu da cutar a ranar Alhamis, wanda ya kawo jimilar wadanda suka kamu da cutar a kasar ta arewacin Afrika zuwa 15,079, ciki har da mutane 242 da suka mutu.

Kasar ta Morocco ta kuma fara sassauta matakan kulle na yaki da COVID-19. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China