Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasashen Morocco da Senegal sun amince su yaki ayyukan ta'addanci dake addabar shiyyar
2019-09-17 09:37:26        cri
A jiya ne, kasashen Morocco da Senegal, suka sake jaddada kudirinsu na goyon bayan matakan kasa da kasa da na shiyya, na ganin bayan ayyukan ta'addanci da tsattauran ra'ayi a yankin Sahel da Sahara.

Bugu da kari, kasashen biyu sun amince su zurfafa hadin kansu a fannin yaki da ta'addanci, ta hanyar musayar muhimman bayanai da kwarewa. Kamar yadda ministocin harkokin wajen kasashen biyu suka bayyana cikin wata sanarwa bayan ganawarsu.

Da suke karin haske, ministan harkokin wajen Morocco Nasser Bourita da takwaransa na Senegal Amadou Ba, sun yaba da dadaddiyar alaka mai inganci dake tsakanin kasashen biyu, da ci gaban da aka samu karkashin hadin gwiwa, musamman a fannonin kiwon lafiya da aikin gona, da sufuri, da kiwon kifi, da kuma diflomasiya. (Ibrahim Yaya)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China