Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sin ta gaji da zargin da Mike Pompeo ke mata ta hanyar amfani da batun annobar COVID-19
2020-07-09 20:30:47        cri
Jiya Laraba, sakataren harkokin wajen kasar Amurka Mike Pompeo ya yi amfani da batun wai gaskiyar matsalar cutar COVID-19, don zargin kasar Sin, cewa jam'iyyar kwaminis ta Sin ba ta da amana, kamata ya yi a dora mata laifi. Game da haka, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian ya bayyana a yayin taron manema labaru da aka shirya a yau Alhamis a nan birnin Beijing, cewa, "ba ka gaji da yin zargi ba, amma mun gaji da saurara."

Zhao ya kara bayyana cewa, idan ana maganar cancanta, a 'yan shekarun da suka gabata, kasar Amurka ta yi amfani da fifikon Amurka a dandalin kasa da kasa, don yin watsi da alkawarin da ta yi da nauyin dake bisa wuyanta, ta yi janyewa daga yarjeniyoyi da hukumomi daban daban, yanzu ta kasance wanda ta fi kowace tada fitina a duniya. Idan ana maganar gaskiya, Zhao ya bayyana cewa, yana son ya tambayi Mike Pompeo ko gwamnatin kasarsa na iya fadar gaskiya kan sansanin nazarin kwayoyin hallitu na Fort Detrick, da "cutar taba ta lantarki", da kuma dakunan gwaje-gwajen kwayoyin hallitu da kasar ta kafa a sassa daban-daban na duniya, ko za ta iya yiwa jama'arta da sauran kasashen duniya wani bayani game da wadannan? Kan batun nauyi kuma, a cikin kasa da rabin shekara, wadanda suka kamu da cutar COVID-19 a kasar sun wuce miliyan 3, wadanda suka rasa rayukansu sakamakon cutar sun wuce dubu 130. Lallai ya kamata gwamnatin kasar Amurka ta dauki alhakin wadannan. (Bilkisu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China