Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Luguden wuta da sojojin Nijeriya suka yi ya yi sanadin mutuwar 'yan bindiga da dama
2020-06-26 13:17:17        cri
Rundunar sojin Nijeriya ta ce dakarunta sun kashe 'yan bindiga da dama tare da lalata maboyarsu, yayin wani luguden wuta ta sama da suka yi a yankin arewa maso yammacin kasar.

Wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce rundunar Operation Hadarin Daji ta kai hari dajin Doumorou dake jihar Zamfara, lamarin da ya kai ga lalata sansanonin 2 na 'yan bindiga.

A cewar hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, fashi da satar mutane don neman kudin fansa da sauran laifuffuka, sun yi kamari a yankin arewa maso yammacin Nijeriya daga farkon shekarar nan.

Rundunar sojin ta ce ayyukanta na baya-bayan nan sun shawo kan lamarin. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China