![]() |
|
2020-06-26 13:17:17 cri |
Wata sanarwa da rundunar ta fitar, ta ce rundunar Operation Hadarin Daji ta kai hari dajin Doumorou dake jihar Zamfara, lamarin da ya kai ga lalata sansanonin 2 na 'yan bindiga.
A cewar hukumar kula da 'yan gudun hijira ta MDD, fashi da satar mutane don neman kudin fansa da sauran laifuffuka, sun yi kamari a yankin arewa maso yammacin Nijeriya daga farkon shekarar nan.
Rundunar sojin ta ce ayyukanta na baya-bayan nan sun shawo kan lamarin. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China