![]() |
|
2020-06-22 10:12:26 cri |
A cewar shugaban hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Lagos, Femi Oke Osanyintolu, fashewar tankoki na farko, ta faru ne da safiyar jiya Lahadi biyo bayan arangamar da tankoki biyu dake shake da mai suka yi a kan gadar Kara dake wajen birnin Lagos.
Baya ga tankokin biyu, gobarar da hatsarin ya haifar, ta shafi wata tanka ta daban da wata babbar motar dakon kaya, wanda ya yi sanadin fashewar tankar.
Hukumar kiyaye haddura ta kasar, ta bukaci direbobi su nemi wata hanya ta daban domin ba masu aikin ceto damar kammala aikinsu a kan gadar Kara. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China