Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Shugaba Xi ya yi kira da a inganta tsarin hadin gwiwar Sin da Philippines
2020-06-12 10:34:34        cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya gabatar da shawarar bullo da sabbin dabaru, da tsare tsare, na inganta hadin gwiwar dake tsakanin kasar sa da Philippines, a gabar da ake fafutukar shawo kan cutar COVID-19, ta yadda sannu a hankali, za a kai ga dawo da musayar muhimman jami'ai, da gaggauta bunkasa cudanya mai alfanu a sassa daban daban.

Shugaban Xi ya yi wannan tsokaci ne, yayin zantawa ta wayar tarho da takwaransa na Philippine Rodrigo Duterte. A yayin tattaunawar, Xi ya ce irin wannan yunkuri, zai taimakawa kasashen biyu, cimma nasarar bunkasa fannonin su na zamantakewar al'umma, da tattalin arziki, ta yadda al'ummun su za su ci gajiya.

A wani ci gaban kuma, shugaban na Sin, ya yi kira da a zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasar sa da Belarus. Shugaban ya yi wannan kira ne yayin zantawa ta wayar tarho da shugaban kasar Belarus Alexander Lukashenko a daren jiya Alhamis.

Xi Jinping ya shawarci sassan biyu, da su yi kokari tare, wajen sauya kalubalen dake addabar su zuwa damammaki, su kuma zurfafa hadin gwiwa wajen cimma nasarar shawarar ziri daya da hanya daya. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China