![]() |
|
2020-06-04 10:42:09 cri |
Jiya Laraba, babbar jami'ar kula da harkokin hakkin dan Adam na MDD Michelle Bachelet ta fidda sanarwa ta biyu kan babbar zanga-zangar da ake yi a kasar Amurka, sakamakon mutuwar wani dan kasar bakar fata, inda jami'a ta bayyana cewa, ya kamata a saurari ainihin bukatun masu zanga-zanga dake cikin birane masu yawa na kasar Amurka, idan ana son kawo karshen matsalar wariyar launin fata da rikice-rikcien da ake fama da su a halin yanzu.
Ta kuma jaddada cewa, ya kamata shugaban kasar Amurka ya yi Allah wadai da kabilanci da wariyar launin fata a ko da yaushe, musammam ma a lokacin da ake samun tashe-tashen hankula, sa'an nan kamata ya yi ya saurari dalilan da suka haddasa fushin jama'a, domin daukar matakai masu dacewa wajen warware matsalar rashin daidaito tsakanin al'umma. (Maryam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China