Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
'Yan siyasan kasar Amurka da suka yi amfani da batun Taiwan wajen haifar da matsala za su janyo wa kansu wulakanci
2020-05-19 20:50:10        cri
Daga jiya Litinin, zuwa yau Talata, an gudanar da taron hukumar lafiya ta duniya WHO, inda aka sake yin watsi da bukatar yankin Taiwan, na neman halartar wannan taro, lamarin da ya kawo karshen yunkurin da wasu 'yan siyasa na kasar Amurka suke yi, na neman gayyato yankin Taiwan ya halarci wannan taro na kasa da kasa. Hakan dai na nufin cewa, ko da yake wasu 'yan siyasa na kasar Amurka, na neman ta da rikici a taron WHO, amma yunkurinta bai samu goyon baya daga al'ummun duniya ba.

Bayan shiga watan Mayu, yanayin yaduwar cutar COVID-19 na kara tsananta a kasar Amurka, lamarin da ya sa wasu 'yan siyasan kasar ke ci gaba da kokarin dorawa kasar Sin laifi, tare da haifar mata da matsala. Don haka ne kuma suka tsara batun "gayyato yankin Taiwan don ya halarci taron hukumar WHO". Inda majalisar gudanarwar kasar Amurka ta nuna goyon baya ga yankin na Taiwan, a shafin sada zumunta na Twitter, sa'an nan majalissun kasar suka yi kira ga gwamnatocin kasashe kimanin 60, da su nuna goyon baya ga Taiwan, har ma majalissar datawan kasar ta zartas da wani kuduri, na sanya sakataren harkokin wajen kasar ya tsara wata dabara, ta taimakawa yankin Taiwan samun matsayi na mai sa ido a cikin hukumar WHO.

Amma hakika su ma wadannan 'yan siyasa na kasar Amurka, sun san cewa, dole ne za su ci tura, duba da cewa, suna neman kalubalantar manufar kasancewar kasar Sin daya tak a duniya. Don gane da wannan batu, Steven Solomon, jami'i mai kula da batun shari'a na hukumar WHO, ya jaddada a kwanan baya cewa, jamhuriyar jama'ar kasar Sin, ita ce wakiliyar al'ummar Sin daya tak, dake da matsayi na halas cikin tsarin MDD, kuma hukumar WHO za ta dauki mataki iri daya da na MDD. (Bello Wang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China