Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An tilasta sanya makarin baki da hanci a Nijeriya yayin da ake tsaka da fama da COVID-19
2020-05-16 16:22:21        cri
Gwamnatin Nijeriya ta bayyana bukatar sanya makarin baki da hanci yadda ya kamata, domin rage yaduwar COVID-19 a kasar.

Darakta janar na cibiyar dakile yaduwar cututtuka da kandagarkinsu ta kasar, Chikwe Ihekweazu, ya bayyana yayin wani taron manema labarai da ya gudana jiya a birnin Abuja cewa, makarin hanci da baki karin mataki ne na kandagarki, kuma bai kamata a maimaita amfani da shi ko kuma mutane biyu su yi amfani da guda daya ba.

Ya ce sanya makarin hanci da baki yadda ya kamata, zai iya kare yaduwar COVID-19.

A watan da ya gabata ne hukumomi a kasar suka tilasta sanya makarin baki da hanci domin dakile yaduwar kwayar cutar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China