Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Ma'aikatar harkokin wajen Sin ta jaddada manufar kasar Sin daya tak kan harkokin WHO
2020-05-12 20:05:58        cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Zhao Lijian, ya bayyana cewa, masana tsare-tsare daga yankin Taiwan na kasar Sin, za su iya shiga a dama da su cikin sauki a ayyukan hukumar lafiya ta duniya karkashin manufar kasar Sin daya tak a duniya.

Kalaman nasa na zuwa ne, bayan da sashen kula da harkokin waje na hukumomin yankin na Taiwan ya sanar a jiya Litinin cewa, a shekarar 2005, babban yankin kasar Sin ya sanya hannu kan wata takardar fahimtar juna ta sirri (MOU) da WHO kan harkokin da suka shafi shigar yankin na Taiwan ayyukan da suka shafi WHO.

Zhao ya jaddada cewa, kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma yankin Taiwan wani bangare na kasar Sin da ba za a iya raba shi ba. Yana mai cewa, kasar Sin ba ta bukatar sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna da duk wata hukumar kasa da kasa na dawo da yankin bangaren kasar Sin.

Ya ce, daga shekarar 2019 zuwa wannan lokaci, rukunoni 16 cikin 24 na masana lafiya daga Taiwan sun shiga ayyukan WHO. Yana mai cewa, yadda mahukuntan yankin Taiwan suke sanya siyasa wajen jirkita batun annobar COVID-19, shirme ne kawai. (Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China