Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An hallaka 'yan Boko Haram 20 yayin musayar wuta da sojojin Najeriya
2020-05-12 09:39:39        cri
Kimanin mayakan Boko Haram 20 sojojin Najeriya suka kashe bayan musayar wuta da suka yi a garin Bama dake jahar Borno a shiyyar arewa maso gabashin Najeriya, wani jami'in yankin ne ya tabbatar da hakan.

Saeed Sambo, shugaban karamar hukumar Gwoza dake jahar, ya ce mayakan 'yan ta'addan da dama sun tsere daga yankin a ranar Lahadi a lokacin fafatawar.

Sambo ya fadawa 'yan jaridu cewa dakarun sojojin sun yi musu rakiya a lokacin da mayakan na Boko Haram suka yi musu kwanton bauna a garin.

Jami'in ya kara da cewa, mayakan sun kaddamar da hare hare masu yawa ta hanyar amfani da ababen fashewa da suke amfani dasu daga bisani suka yi harbe harbe. Sai dai kuma, dakarun sojojin sun mayar musu da martani mai tsanani.

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China