2020-05-11 15:58:58 cri |
Ko shakka babu kasar Sin ta kasance daya daga cikin manyan abokan kasuwancin Najeriya mafi girma a fadin duniya, kana harkokin cinikayyar bangarorin yana kara fadada zuwa sauran fannoni. Layin dogo na Legas zuwa Ibadan zai fara aiki nan bada jimawa ba, aikin gina yankin kasuwanci cikin 'yanci yana gudana cikin sauri, bugu da kari aikin gina matatar mai ta Dangote da ma sauran ayyuka masu muhimmanci da kamfanonin kasar Sin suka zuba jari a Najeriya suna kara bunkasuwa a kullum.
Bangarorin biyu suna kara cudanya da juna kuma suna cin babbar moriyar hadin gwiwar dake tsakaninsu. Suna kara zurfafa hadin gwiwar moriyar juna tsakanin kasashen biyu da kuma al'ummominsu. Yanzu muhimmin lokaci ne na bunkasa danganatakar abota dake tsakanin Najeriya da Sin da fadada hadin gwiwa, duk wani yunkuri na kawo illa da koma baya game da hadin gwiwar bangarorin biyu, tilas ne a dakile shi.
Matakan kandagarkin yaki da annobar COVID-19 a birnin Guangzhou yana da alaka da irin dangantakar dake tsakanin jama'ar Najeriya dake zaune a kasar Sin. Babban tushen da ya haifar da matsalar shi ne rashin kyakkyawan tsarin sadarwa tsakanin bangarorin biyu.
Dukkan sassan biyu wato gwamnatin Najeriya da gwamnatin kasar Sin sun yi dukkan kokarin da ya dace domin warware matsalar don kare matsayin hadin gwiwar moriyar juna da kuma cimma nasarar bunkasuwar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.(Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China