Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kafofin watsa labaran Afirka: Amurka na bata dangantakar dake tsakanin Sin da Afirka
2020-05-11 13:07:30        cri
Kwanan baya, manyan kafofin watsa labaran kasashen Afirka sun bayyana cewa, kasar Amurka tana zargin kasar Sin da kasancewa asalin cutar numfashi ta COVID-19 da dai sauransu, domin karkatar da hankalin jama'a daga gazawarta wajen fuskantar aikin dakile yaduwar cutar numfashi ta COVID-19 cikin kasar Amurka yadda ya kamata, da kuma bata dangantakar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka.

A ranar 7 ga wata, jaridar The Standard ta kasar Kenya, ta wallafa sharhin babban jami'in sakatariyar majalisar raya wuraren yankin iyaka na kasar Mohamed Guleid, inda ya bayyana cewa, zargin da kasar Amurka ta yi wa kasar Sin kan asalin cutar COVID-19, ya nuna cewa, kasar Amurka tana son tada yaki tsakaninta da kasar Sin. Ya kara da cewa, ainihin sabanin dake tsakanin Sin da Amurka ba cutar COVID-19 ba ce, batu ne na bunkasuwar kasar Sin cikin sauri.

Har wa yau, manyan kafofin yada labarai na kasashen Afirka da suka hada da kamfanin dillancin labaran kasar Habasha, jaridar Punch ta Najeriya, da gidan talabijin na kasar Afirka ta Kudu da sauransu, sun mai da hankali kan jayayyar dake tsakanin kasar Sin da kasar Amurka, kan batun asalin cutar numfashi ta COVID-19, inda suka kuma jaddada cewa, gwamnatin kasar Amurka ta yiwa kasar Sin wannan zargi a daidai lokacin da ake zarginta kan gaza yin aikin dalike yaduwar cutar yadda ya kamata, shi ya sa, 'yan adawar gwamnatin kasar Amurka sun nuna cewa, Donald Trump yana zargin kasar Sin ne kawai, domin dauke hankalin jama'ar kasarsa.

Haka kuma, jaridar Leadership ta Najeriya, da jaridar The Reporter ta kasar Habasha, da kamfanin dillacin labaran kasar Habasha, da jaridar The Star ta kasar Afirka ta Kudu, da wasu manyan kafofin watsa labaran kasashen Afirka, sun yi kira da a karfafa hadin gwiwar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka wajen yaki da cutar. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China