Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Iran tayi baranzar rusa yarjejeniyar nukiliya idan MDD ta tsawaita takunkumin makamai karkashin matsin lambar Amurka
2020-05-03 17:16:43        cri
Wani babban jami'in tsaron Iran ya bayyana cewa, yarjejeniyar nukilyar Iran ta 2015 mai cike da tarihi, wacce kasa da kasa suka mata lakabin hadaddiyar yarjejeniyar hadin gwiwa ta (JCPOA), zata zo karshe muddin MDD ta goyi bayan tsawaita wa'adin takunkumin makamai da aka kakabawa Iran karkashin matsin lambar Amurka.

Ali Shamkhani, sakataren majalisar koli kan al'amurran tsaron Iran ya wallafa a shafin twita na majalisar a yau Lahadi cewa, yarjejeniyar JCPOA zata mutu har abada ta hanyar yin watsi da kudurin kwamitin tsaron MDDr mai lamba 2231 idan haramtaccen takunkumin makaman Iran ya cigaba.

Shamkhani, ya bukaci kasashen Turai masu ruwa da tsaki kan yarjejeniyar su dauki matakai kan yarjejeniyar game da matsin lambar Amurka.

Sakataren harkokin wajen Amurka Mike Pompeo ya ce, Washington tana duba yiwuwar bin dukkan hanyoyin da suka dace na sabunta takunkumin hana Iran cinikin makamai wanda wa'adinsa zai kare nan da watanni shida masu zuwa.

A ranar Asabar gwamnatin Iran ta yi barazanar cewa, muddin aka tsawaita takunkumin makaman Iran, za'a fuskanci mummunan martani daga kasar. (Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China