![]() |
|
2020-04-20 09:37:29 cri |
Da yake Karin haske cikin wata sanarwa da kamfanin dillacin labarai na Xinhua na kasar Sin ya samu kwafenta a Abuja, fadar mulkin Najeriya, mai magana da yawun ma'aikatar tsaron kasar John Enechen, ya bayyana cewa, babu wani soja da ya rasa ransa ko makamansu yayin bata kashin.
A wani labarain kuma, kakakin ya kara da cewa, a wannan rana dakarun kasar sun yi nasarar kama wasu 'yan bindigar dake addabar mazauna wasu kauyuka a jihar Katsina dake yankin arewa maso yammacin kasar.
Jami'in ya ce, dakarun sun dakile wani hari da 'yan bindigar suka shirya kaiwa mazauna kauyukan Kurechi da Qurzan Maikuka a karamar hukumar Dutsin-Ma dake jihar Katsina, inda suka kama wasu daga 'yan bindigar yayin wasu suka tsere da raunuka a jikinsu. (Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China