Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
WHO ta bayyana damuwa game da yanayin da wasu kasashe ke ciki yayin da wadanda suka kamu da cutar COVID-19 ya dara miliyan 2 a duniya
2020-04-18 16:45:45        cri
Darakta Janar na hukumar lafiya ta duniya (WHO) Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce duk da ana samu sakamako masu karfafa gwiwa a wasu kasashe, yanayin da wasu kasashe ke ciki na haifar da damuwa, yayin da adadin wadanda aka tabbatar sun kamu da cutar COVID-19 a duniya ya dara miliyan 2.

Da yake jawabi yayin wani taron manema labarai ta kafar bidiyo daga Geneva a jiya, Tedros Ghebreyesus, ya ce cikin makon da ya gabata, an samu karuwar kaso 51 na wadanda suka kamu da cutar a Afrika, yayin da aka samu karuwar kaso 60 na wadanda suka mutu a nahiyar.

Ya ce la'akari da kalubalen da ake fuskanta na samun kayayyakin gwaji, akwai yiwuwar ainihin adadin ya zarce wanda aka bayar.

A cewarsa, da taimakon WHO, yanzu galibin kasashen Afrika na iya gwajin cutar, sai dai har yanzu akwai gibi sosai na samun kayayyakin gwajin.

Har ila yau, ya ce suna aiki da abokan huldarsu wajen cike wannan gibi da kuma taimakawa kasashen Afrika yaki da cutar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China