Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Babban magatakardan MDD: Dole ne a goyi bayan WHO
2020-04-15 11:07:51        cri
Shugaban kasar Amurka Donald Trump, ya sanar a jiya Talata cewa, kasarsa za ta dakatar da biyan kudin kasancewar ta mamba a hukumar kiwon lafiyar ta duniya WHO.

Dangane da wannan batu, babban magatakardan MDD Antonio Guterres, ya bayyana a jiya cewa, dole ne a goyi bayan hukumar kiwon lafiyar WHO, wadda ke da muhimmiyar ma'ana ga kasa da kasa, wajen cimma nasarar yaki da cutar numfashi ta COVID-19.

Kafin haka kuma, kasar Amurka ta zargi hukumar WHO, ta kuma sanar da dakatar da biyan kudin kasancewar ta mamba a hukumar. Dangane da wannan batu, a ranar 8 ga watan nan, babban sakataren hukumar WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya ce, bai dace a mai da annobar cutar numfashi ta COVID-19 a matsayin sharadin siyasa ba, kuma ya kamata wurare daban daban a matakin kasa, da ma sassan kasa da kasa su yi hadin gwiwa wajen yakar annobar. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China