Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
WHO ta shawarci kasa da kasa su dauki muhimman matakai don dakile cutar COVID-19
2020-03-26 11:18:29        cri

Babban daraktan hukumar kiwon lafiya ta duniya WHO Tedros Adhanom Ghebreyesus, ya bayyana a jiya Laraba cewa, baya ga daukar matakai na rage cudanyar jama'a da kara nisanta tsakanin mutane, ya kamata kasashen duniya su dauki muhimman matakai a fannoni 6 domin hana yaduwar cutar numfashi ta COVID-19, ta yadda ba za a dawo da cutar ba, bayan da aka soke dukkanin matakan hana yaduwar cutar.

Bisa sabon rahoton da WHO ta fidda a jiya Laraba, an ce, ban da kasar Sin, adadin mutanen da aka tabbatar sun kamu da cutar numfashi ta COVID-19 ya kai 332331, yayin da mutane 15153 suka rasa rayukansu. Kana, gaba daya akwai mutane 413467 da aka tabbatar sun kamu da cutar a duk fadin duniya, yayin da mutane 18433 suka mutu, kuma annobar ta shafi kasashe da yankuna har guda 196. (Maryam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China