Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Najeriya: An samu rasuwar mutum na farko sakamakon harbuwa da cutar COVID-19
2020-03-23 19:32:59        cri
Hukumomin lafiya a Najeriya sun sanar da rasuwar mutum na farko dake dauke da cutar numfashi ta COVID-19 a Litinin din nan.

A cewar cibiyar dakile yaduwar cututtuka ta kasar NCDC, mutumin mai shekaru 67 da haihuwa ya dawo kasar ne daga Birtaniya inda ya je domin neman magani.

Cibiyar ta ce baya ga cutar ta COVID-19 mutumin na fama da wasu cututtukan da suka hada da sankarar da suka shafi kananan halittun jini da ciwon suga, shi ya sa yake jinyar sankara.

Kawo yanzu, Najeriya ta samu wadanda suka kamu da cutar COVID-19 kimanin 36 a kasar. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China