2020-03-16 09:47:25 cri |
Mukaddashin shugaban hukumar ba da agajin gaggawa ta kasar, Ibrahim Farinloye, wanda ya tabbatar da adadin gawarwakin ga kamfanin dillancin labarai na Xinhua, ya ce gobarar ta tashi ne da misalin karfe 9 na safiyar jiya Lahadi, agogon kasar. Ya ce wajen lamarin ya auku na kusa da kwalejin 'yan mata ta Bethlehem, inda sama da dalibai 60 na kwalejin suka ji raunika daban-daban, kuma tuni aka garzaya da su asibitin rundunar sojin ruwan kasar.
A cewarsa, daga bisani, gobarar da ta tashi, ta yadu zuwa bututun man kamfanin mai na kasar dake yankin, sai dai an kulle bututun a wani mataki na kandagarki.
A nasa bangaren, darakta janar na hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Lagos, Olufemi Oke-Osanyintolu, ya ce gwamnati za ta gudanar da cikakken bincike domin gano musabbabin gobarar. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China