![]() |
|
2020-03-09 19:38:38 cri |
NCDC ta ce ana ci gaba da gwada dukkanin wadanda suka yi cudanya da mutum na farko da ya shiga kasar dauke da cutar, a wani mataki na dakile yaduwar ta. Ana kuma ci gaba da killace mutanen 2 da ake da tabbacin sun harbu da cutar.
Mutum na farko dai baturen Italiya ne, wanda ya shiga Najeriya a ranar 25 ga watan Fabarairu daga birnin Milan, ya kuma shiga kasar ne domin ziyarar kasuwanci ta dan lokaci, kafin daga bisani a gano yana fama da cutar ta COVID-19. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China