![]() |
|
2020-03-14 16:39:48 cri |
Donald Trump ya ce ya ba sakataren harkokin lafiya da hidimtawa jama'a na kasar, ikon dage wasu dokoki da ka'idoji, da nufin tabbatar da dakile cutar COVID-19 tare da kula da marasa lafiya.
Ya kara da cewa, yana umartar dukkan jihohin kasar su kafa cibiyoyin ayyukan gaggawa domin taimaka musu yaki da cutar.
A cewar cibiyar nazarin tsarukan kimiyya da aikin injiniya ta jami'ar Johns Hopkins ta kasar, ya zuwa ranar Alhamis, Amurka ta bayar da rahoton samun mutane 1,663 da suka kamu da cutar COVID-19, inda a kalla mutane 40 suka mutu. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China