![]() |
|
2020-03-10 20:00:08 cri |
Geng Shuang ya ce a yau, kasashen Afirka da al'ummun su, na tare da kasar Sin a wannan yaki, wanda hakan ya nuna irin kawance da 'yanuwantaka dake haifar da taimakon juna tsakanin sassan biyu.
Geng ya kara da cewa, a halin yanzu, kasashen Afirka na fuskantar barazanar yaduwar cutar, tuni kuma cutar ta bulla a wasu kasashen nahiyar. Don haka Sin a shirye take, ta karfafa matakan ta na kandagarkin yaduwar wannan cuta, da karfafa hadin gwiwa da taimako ga nahiyar Afirka. Kaza lika za ta samar da tallafin kwarewa, da ba da agaji da ya dace, a fannin ayyukan kiwon lafiya da kare hadurra, a matakin yankuna da na kasa da kasa. (Saminu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China