2020-03-07 16:32:39 cri |
Ministan lafiya na kasar, sagie Ehanire, ya shaidawa wani taron manema labarai jiya a Abuja cewa, har yanzu ana bibiyar mutane 21 da mai cutar ya yi mu'amala da su a Lagos, da kuma wasu 40 da ya yi mu'amala da su a jihar Ogun dake makwabtaka da Lagos din.
Ya kara da cewa, gwamnatin Nijeriya ta zage damtse wajen kare yaduwar cutar ta hanyar cibiyar shiryawa tunkarar annoba a bangarori daban daban, dake karkashin hukumar dakile yaduwar cututtuka ta kasar wato NCDC.
Kawo yanzu, Nijeriya ta kafa dakunan gwaji 5 dake iya gwajin cutar COVID 19 a cikin kasar. (Fa'iza Mustapha)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China