Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Karon farko Kamaru ta bada rahoton bullar cutar COVID-19
2020-03-06 20:49:54        cri
Ma'aikatar kiwon lafiya ta kasar Kamaru ta tabbatar da bullar cutar numfashi ta COVID-19 a karon farko a kasar yau Jumma'a.

Gidan talabijin na kasar Kamaru CRTV ya ruwaito sanarwar ma'aikatar dake cewa, wanda ya kamu da cutar, wani dan asalin kasar Faransa ne, mai shekaru 58 a duniya, wanda ya isa birnin Yaounde a ranar 24 ga watan Fabrairu.

Sanarwar ta kara da cewa, an riga an killace dan Faransan don ba shi magani a babban asibitin Yaounde, kuma an bukaci al'ummar kasar su yi taka-tsantsan da mutunta ka'idojin kiwon lafiya.(Murtala Zhang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China