2020-02-28 13:24:56 cri |
Dan kasar Italiya da ya kamu da cutar, yana aiki ne a Nijeriya, ya koma Lagos daga birnin Milan na Italiya a ranar 25 ga wata. Dakin gwaje-gwaje na sashen nazarin kwayoyin cuta na asibitin jami'ar Lagos ya tabbatar da cewa, mutumin ya kamu da annobar. Yanzu haka yana samun jiyya a asibitin shawo kan cututtuka masu yaduwa a Yaba da ke Lagos, kuma ba ya cikin hali mai tsanani.
Gwamnatin Nijeriya tana inganta matakanta na kandagarki da dakile yaduwar annobar. Cibiyar kandagarki da hana yaduwar annoba ta Nijeriya NCDC tana jagorantar hukumomin yaki da cutar COVID-19 wajen daukar matakan gaggawa, za kuma ta hada kai da hukumar lafiya ta Lagos don daidaita barkewar annobar da kuma daukar matakai.
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China