![]() |
|
2020-02-28 10:55:10 cri |
Wakiliyar hukumar ta WHO a nahiyar Afirka, Tereza Kasaeva, wadda ta bayyana hakan yayin da ta jagoranci wata tawaga a lokacin da ta ziyarci shugaban majalisar dattawan Najeriya a Abuja, fadar mulkin kasar, ta bayyana cewa, cutar ta yi sanadiyar mutuwar sama da mutane miliyan 1.5 a duniya a shekara.
Kaseava ta yi kira ga gwamnatin Najeriya, da ta kara samar da kudade a ayyukan kiwon lafiya a matakin farko, ta hanyar daukar matakan gaggawa a bangaren majalisar dokokin kasar.
A cewar jami'ar, hukumar WHO za ta ci gaba da amfani da duk wasu matakan ta na fadakar da jama'a, don kara samar wa Najeriya, kasa mafi yawan al'umma a nahiyar Afirka da kudade da tsare-tsaren da ake bukata, yayin da ta ke kokarin ganin bayan cutar tarin fuka a fadin kasar nan da shekarar 2030.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China