![]() |
|
2020-02-26 09:47:13 cri |
Da yake jawabi ta tashar talabijin na ENTV ta kasar, Abderrahmane Benbouzid, ya ce wanda ya kamu da cutar dan kasar Italiya ne da ya isa Algeria a ranar 17 ga watan Fabreru tare da wani mutum, yana mai cewa tuni aka tura su asibitin Pasteur na birnin Algiers. Kuma bayan bincike, an tabbatar da daya daga cikinsu na dauke da cutar numfashi ta COVID-19.
Ya kara da cewa, nan take aka kebe mara lafiyan, inda ake ba shi kulawa ta musammam.
Har ila yau, ministan ya tabbatar da cewa an dauki matakan kariya a filayen jiragen sama da tasoshin ruwa da iyakokin kasa, ciki har da kafa kamarori masu auna zafin jiki. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China