Xi: Sin na ba da muhimmiyar gudunmawa a fannin kiwon lafiyar al'ummar duniya
A Yau Talata ne shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya zanta ta wayar tarho da yarima mai jiran gado, na masarautar hadaddiyar daular Larabawa Sheikh Mohammed bin Zayed Al Nahyan. Yayin tattaunawar tasu, shugaba Xi ya ce bisa buri na tabbatar da kafuwar al'umma mai makoma guda ga dukkanin bil Adama, baya ga kokarin da take yi na kare rayuka da lafiyar al'ummunta, a hannu guda kuma, kasar Sin na ba da muhimmiyar gudummawa, ga ayyukan kare lafiyar al'ummar duniya baki daya. (Saminu Hassan)
Labarai masu Nasaba