Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Sojojin Najeriya sun lalata sansanin horas da mayakan Boko Haram
2020-02-19 10:52:56        cri
Kakakin rundunar sojojin saman Najeriyar ya ce, wasu hare haren ta jiragen sama da rundunar sojojin saman Najeriya suka kaddamar ya lalata wani sansanin horas da mayakan Boko Haram a shiyyar arewa maso gabashin kasar.

Ibikunle Daramola, mai magana da yawun rundunar sojojin saman Najeriya ya ce sansanin da aka lalata a yankin Tumbun Zarami, dake daura da kan iyakar tafkin Chadi a jihar Borno a shiyyar arewa maso gabashin kasar, kakakin ya ce sun yi nasarar tarwatsa sansanin ne a ranar Lahadi.

Daramola ya ce, an kaddamar da hare haren ne bayan kammala ayyukan bincike a shiyyar na tsawon kwanaki, inda aka gano hakikanin yankunan, da samun cikakkun bayanan sirri daga majiyoyi masu yawa, ciki har da hedkwatar dakarun rundanar wanzar da tsaron hadin gwiwa.(Ahmad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China