2020-02-17 21:06:18 cri |
Yayin taron, an jaddada cewa, dole ne a kara karfafa aikin tantance mutanen da ake zaton sun kamu da cutar a birnin Wuhan da biranen dake fadin lardin Hubei, tare kuma da samar musu da karin gadajen jinya, haka kuma gwamnatin kasar za ta kara tura ma'aikatan jinya zuwa wuraren domin ba su kulawa, ta yadda za a ceto rayukan wadanda cutar ta yi tsanani a jikinsu, a sa'i daya kuma, ya zama wajibi a tabbatar da lafiyar ma'aikatan jinya, tare kuma da samar musu isassun kayayyaki da na'urorin da suke bukata.(Jamila)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China