![]() |
|
2020-02-15 15:59:43 cri |
Yayin wani taron manema labarai na mako-mako a hedkwatar Tarayyar dake Addis Ababa na Habasha, daraktan cibiyar, Dr. John Nkengasong, ya ce cibiyar na gudanar da tsare-tsare da ayyuka, kan yadda nahiyar za ta shirya tare da tunkarar yuwuwar barkewar cutar Corona.
Cibiyar wadda ta hada kwararru daga fadin nahiyar, daga kasashe 5 da suka hada da Senegal da Kenya da Morocco da Nijeriya da Afrika ta Kudu, za ta mayar da hankali kan fannonin 5 da za ta sawa ido, wadanda suka hada da matakan kariya da na dakile yaduwar cutar da jinyar wadanda suka kamu da bada bayanan hadduran da za a iya fuskanta da kuma kula da lafiyar al'umma. (Fa'iza Mustapha)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China