Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Shugaban Afrika ta kudu ya karbi ragamar shugabancin karba-karba na AU
2020-02-10 09:17:47        cri

Shugaban Afrika ta kudu Cyril Ramaphosa, ya karbi ragamar shugabancin karba-karba na Tarayyar Afrika (AU), yayin bude taron shugabannin kasashe da gwamnatoci na tarayyar da ya gudana jiya a hedkwatarta dake birnin Addis Ababa na Habasha.

Taken taron karo na 33 dake gudana a kasar dake gabashin Afrika shi ne "Kawar da makamai: samar da kyakkyawan yanayi ga ci gaban Afrika."

Cyril Ramaphosa ya karbi ragamar shugabancin ne daga hannun shugaban Masar, Abdel Fattah al-Sisi.

Da yake jawabin karbar ragamar, shugaba Ramaphosa ya ce zai yi kokarin inganta batutuwan da Afrika ta sa a gaba na samun ci gaba da zaman lafiya, ta hanyar kara zurfafa dangantaka tsakanin kasashe mambobin tarayyar. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China