![]() |
|
2020-02-09 17:09:58 cri |
A game da taron kolin kungiyar da za a fara a yau, ya ce taken taron shi ne "Kawar da hare-haren bindiga, don samar da kyakkyawan yanayin ci gaban nahiyar Afirka", taron zai mayar da hankali kan batutuwan zaman lafiya da tsaro a nahiyar Afirka. A ganinsa, kasar Sin tana taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da zaman lafiya da bunkasuwa a duniya, kuma fasahohin da kasar ta samu ya dace kasashen Afirka su yi koyi.
Mr.Thomas Kwesi Quartey ya kuma bayyana godiya ga kasar Sin bisa gudummawar da ta samar ga kasashen Afirka, ya ce kungiyar tarayyar Afirka tana son ci gaba da gudanar da hadin gwiwa da kasar Sin ta fannoni da dama. (Lubabatu)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China