Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
An kashe mutane 7 a hari kan rumfunan zabe a yankin magana da Turanci a Kamaru
2020-02-10 13:05:12        cri

Rundunar sojojin kasar Kamaru ta sanar cewa an kashe mayakan 'yan aware 7 a ranar Lahadi a lokacin da suka yi yunkurin kaddamar da hari kan rumfunan zabe a shiyyar kudu maso yammacin yankin Kamaru mai magana da yaren Turanci.

Lamarin ya faru ne a garin Bangem a lokacin gudanar da zabukan 'yan majalisun dokokin kasar da na kananan hukumomi wadanda aka gudanar a ranar Lahadi a kasar ta shiyyar tsakiyar Afrika. Zabukan da aka gudanar a karon farko tun bayan shekaru bakwai bayan jinkirin da aka samu har sau biyu.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China