Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Yan sandan Kamaru sun bankado yadda ake safarar kananan yara tare da ceto wasu yaran biyu
2020-01-21 10:43:53        cri
Jami'an 'yan sandan jamhuriyar Kamaru sun sanar da cewa sun yi nasarar wargaza hanyar da ake safarar kananan yara inda ake cinikin yaran daga shiyyar kudancin kasar ana sayar da su ga masaya dake kan iyakar kasar da Equatorial Guinea mai makwabtaka da Kamaru.

A Juma'ar da ta gabata, sojojin kurfau na Jamhuriyar Kamaru dake aikin sintiri akan iyakokin kasar sun damke wata motar bas da ake zargi a yankin dake makwabtaka da Equatorial Guinea. sojojin sun yi nasarar kama mutune uku da ake zargin, ciki har da wasu mata da miji da wani mai yin garkuwa, inda suka ceto yara kanana biyu da aka yi garkuwa da su, 'yan tsakanin shekaru 3 zuwa 10 da haihuwa.

Yaran biyu an yi garkuwa da su ne a ranar Alhamis din data gabata, wata mace mai matsakaitan shekaru ce ta yi garkuwar da su, kana ta amsa laifinta a lokacin da ake mata tambayoyi cewa wasu ma'aurata ne suka yi mata alkawarin biyanta kudi kimamin CFA 1,800,000 kwatankwacin dala 3,000 a kan yaran biyu.

Tuni aka sada yaran da iyalansu, kuma suna cikin koshin lafiya, kamar yadda jami'an tsaron suka tabbatar, jami'an sun kara da cewa, tuni aka kaddamar da shirin binciken a hukumance domin wargaza duk wani shirin hadin gwiwar safarar kananan yara akan iyakokin kasar. (Ahmnad)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China