Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Tsohuwar babbar darektar WHO ta yabawa kasar Sin kan yadda take kokarin dakile annoba
2020-02-02 20:14:42        cri
A kwanakin baya, hukumar lafiya ta duniya WHO ta bayyana annobar cutar numfashi ta "Novel Coronavirus Infection" a matsayin "PHEIC", wato "wani batu na gaggawa da ya shafi lafiyar jama'a wanda ya janyo hankalin al'ummun kasashe daban daban". Dangane da batun, Madam Margaret Chan Fung Fu-chun, tsohuwar babbar darektar hukumar WHO, ta bayyanawa wakilin CMG a yau Lahadi cewa, hakan ba ya nufin cewa hukumar WHO ba ta da imani kan gwamnatin kasar Sin game da aikinta na dakile cutar numfashi mai yaduwa ba ne, akasin haka, an yarda da matakan da kasar Sin ta dauka na kokarin sauke nauyin dake bisa wuyanta don taimakawa sauran kasashe.

A cewar Madam Margaret Chan, bayan barkewar cutar numfashin, gwamnatin kasar Sin ta dauki kwararan matakai ba tare da wani jinkiri ba, haka kuma tana bayyana dukkan bayanan da ta samu a fili. Yanzu dukkan jama'ar kasar Sin na kokarin taimakawa aikin dakile cutar numfashin, karkashin jagorancin gwamnatin kasar, wannan a cewar Madam Chan ba wani abu da aka saba gani a sauran kasashen duniya ba ne.

Ban da haka Madam Chan ta jinjinawa masu nazarin kimiyya da fasaha na kasar Sin, inda ta ce masanan kasar Sin sun yi nazari kan kwayoyin cutar "Novel Coronavirus", gami da samun cikakkun bayanansu cikin sauri. Sa'an nan sun raba sakamakon nazarin ga hukumar WHO gami da takwarorinsu na kasashe daban daban. Ta haka sun taimakawa masanan kasashe daban daban fahimtar halayyar musamman ta kwayoyin cutar da suka haddasa annoba a wannan karo. (Bello Wang)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China