![]() |
|
2020-01-29 16:25:25 cri |
Da take karin haske kan haka, minista Gina ta ce, a mako mai zuwa ne, jami'ai daga sashen cinikayya da masana'antun kasar gami da wasu 'yan kasuwa a fannonin aikin gona, da kayayyakin more rayuwa, hakar ma'adinai da magunguna su 40, za su yi kokarin kulla yarjeniyoyi a kasashen biyu.
Ziyarar za ta samarwa kamfanonin Afirka ta Kudun wani dandalin cin gajiya a fannonin cinikayya da zuba jari a kasashen Ghana da Najeriya. Bugu da kari, ziyarar wani bangare ne na karfafa cinikayya tsakanin kasashen nahiyar, yayin da kasashen nahiyar ta Afirka da dama suka sanya hannu kan yarjejeniyar cinikayya marar shinge ta nahiyar.(Ibrahim)
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China