![]() |
|
2020-01-03 09:08:59 cri |
Wata sanarwar da rundunar sojojin kasar ta fitar ta bayyana cewa, hadarin ya rustsa da ma'aikatan jirgin 7, da alkalai 3, da wasu fararen hula 8 ciki har da kananan yara 4. Yanzu haka an fara gudanar da bincike don gano musabbabin hadarin.
Da farko dai jirgin ya kaiwa kungiyar Red Crescent ta Sudan dake El Geneina,babban birnin jihar yammacin Darfur kayayyakin kiwon lafiya ne. A 'yan kwanakin da suka gabata dai, birnin El Geniena ya sha fama da fadan kabilancin da ya yi sanadiyar mutuwa ko jikkatar mutane da dama.(Ibrahim)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China