Tashar samar wutar lantarkin Masar da Sudan za ta fara aiki a watan Janairu
2019-12-30 15:42:50 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar samar da wutar lantarki da makamashin da ake sabuntawa ta kasar Masar Ayman Hamza, ya bayyana cewa, tashar samar da wutar lantarki ta hadin gwiwa tsakanin Masar da Sudan, za ta fara aiki a ranar 12 ga watan Janairun sabuwar shekara, inda ake fatan za ta fara samar da wutan da ya kai megawatts 50.
Ya ce, karfin wutar lantarkin da za ta samar ya kai Kv 220, za kuma ta samar da wutan da ya kai nisan kilomita 1,000.(Ibrahim)