2019-12-27 09:58:44 cri |
Babu wata kungiyar da ta yi ikirarin alhakin kai harin.
A 'yan shekarun baya bayan nan, kungiyoyi masu tsattsauran ra'ayi da 'yan ta'adda masu alaka da kungiyar IS masu tsattsauran ra'ayi, sun sha kaddamar da hare hare a sassan yammacin Jamhuriyar Nijar dake makwabtaka da kasashen Mali da Burkina Faso, lamarin da yayi sanadiyyar hasarar rayuka masu yawa. Ko a ranar 10 ga wannan watan na Disamba kimanin sojojin Nijar 70 aka kashe kana wasu sojojin sama da 10 sun bace a wani harin da 'yan ta'adda suka kaddamar a sansanin sojojin a shiyyar yammacin jamhuriyar Nijar. (Ahmad Fagam)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China