![]() |
|
2019-12-08 16:51:41 cri |
A yayin da yake ziyara a kasar Sin, Mansour ya taba ziyartar yankin Xinjiang sau biyu, game da yanayin yankin, ya bayyana cewa, ana samun zaman lafiya da wadata a yankin Xinjiang a halin yanzu domin gwamnatin yankin da jama'ar yankin sun yi kokari tare don samun bunkasuwa tare.
Mansour ya nuna yabo ga cibiyar horar da fasahohin sana'a da aka kafa a yankin Xinjiang. A ganinsa, ya kamata a tabbatar da hakkin bil Adama na jama'ar yankin don kawar da mugun tasirin da ta'addanci da tsattsauran ra'ayi suka kawo musu, ta hakan za a samu zaman lafiya mai dorewa a yankin. (Zainab)
| ||||
® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China