Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Alakar Sin da Masar ta shiga lokaci mai muhimmanci
2019-12-06 10:26:34        cri
Jakadan kasar Sin a kasar Masar Liao Liqiang, ya bayyana cewa, hadin gwiwa tsakanin kasashen biyu wato Sin da Masar ta shiga wani muhimmin lokaci.

Jakada Liao, ya shaidawa taron manema labarai da aka shirya a ofishin jakadancin Sin dake birnin Alkahira cewa, a 'yan shekarun nan, an samu ci gaba sosai a hadin gwiwar dake tsakanin Masar da Sin bisa manyan tsare-tsare. A mataki na siyasa, a shekarar da ta gabata, manyan jami'an sassan biyu sun ziyarci juna a lokuta daban-daban.

Ya ce, a shekarar 2019 da muke ciki, kusan tawagogin kasar Sin 30 ne suka ziyarci kasar Masar, yayin da ita kuma kasar Masar ta aika tawagogi 20 zuwa kasar Sin. Wadannan ziyarce-ziyarce tsakanin sassan biyu, sun shafi fannonin cinikayya da aikin gona da fasahar kere-kere da binciken kayayyakin tarihi.

Liao ya kara da cewa, a 'yan shekarun nan, alakar Sin da Masar a fannin cinikayya da tattalin arziki ta bunkasa matuka, inda ya ba da misali da yankin masana'antu na TEDA da aikin gina babban yankin kasuwanci dake tsakiyar sabon birnin Masar, a matsayin misali na kyakkyawar alakar dake tsakanin sassan biyu. (Ibrahim Yaya)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China