Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Jami'an Sin da Afrika sun tabbatar da yin hadin gwiwa ga shirin samar da dawwamamman cigaba
2019-12-07 15:48:23        cri
Jami'an kasashen Sin da Afrika sun jaddada aniyarsu na karfafa hadin gwiwar dake tsakaninsu da hadin gwiwar Sin da Afrika a dukkan fannoni, domin tabbatar da cimma nasarar shirin samar da dawwamamman cigaba don amfanawa juna karkashin tsarin mutunta juna da cin moriyar juna.

A taron kasa da kasa na wuni biyu wanda aka kaddamar a ranar Juma'a a helkwatar kungiyar AU dake Addis Ababa na kasar Habasha, an kara jaddada yin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afrika domin tabbatar da bunaksa shirin samar da dawwamamman cigaba.

A jawabinsa na bude taron, jakadan kasar Sin a AU, Liu Yuxi, ya nanata aniyar kasar Sin na cigaba da zurfafa hadin gwiwarta da yin hulda da Afrika don tabbatar da samun kyakkyawan sakamako karkashin tsarin mutunta juna da cin moriyar juna.

Wakilin ya ce, kasar Sin za ta cigaba da bayar da goyon baya da tallafawa Afrika a kokarin da nahiyar ke yi wajen fadada hanyoyin cigaban tattalin arziki, da bunkasa masana'antu, da inganta ayyuka a nahiyar, musamman wajen ba da fifiko game da raya cigaban tattalin arzikin nahiyar Afrika ta fannin aikin gona. (Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China