Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Minista a Najeriya ta yi kira a yanke hukunci mai tsauri kan masu yin lalata da yara
2019-12-05 11:06:10        cri
Ministar kula da harkokin mata a tarayyar Najeriya Pailine Tallen, ta yi kira da a rika yanke hukunci mai tsauri kan masu cin zarafin mata ta hanyar lalata, a wani mataki da kawo karshen yiwa mata fyade da ma dukkan laifukan cin zarafin mata da kananan yara. Kuma hakan na iya zama izna.

Uwargida Tallen ta yi wannan kiran ne, mako guda bayan da hukumar yaki da fataucin bil-Adam ta kaddamar da wani gangamin ilimantar da jama'a, game da yaki da masu cin zarafin mata ta hanyar lalata, ta hanyar kaddamar da wani kundin da za a rika wallafa sunayen mutanen da ke aikata wannan danyen aiki.

Ta bayyana cewa, a kalla kananan yara mata 'yan Najeriya miliyan 2 ne suke fuskantar cin zarafi ta hanyar lalata a shekara, kuma kaso 28 cikin 100 ne kawai na wannan adadi suka kai rahoto.

A don haka ta ce, ya dace a rika zartar da hukunci mai tsanani kan masu aikata wannan laifi. Ta kuma yi kira ga kafofin watsa labarai, da su rika ba da rahoton batutuwan da suka shafi mata, yara da mutane masu rauni.

Wani rahoto da asusun tallafawa yara na MDD (UNICEF) ya fitar, na nuna cewa, 1 cikin 4 na yara mata da kuma yaro daya cikin 10 a Najeriya, sun taba fuskantar cin zarafi ta hanyar lalata.(Ibrahim)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China