Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Macron ya ce Faransa za ta sauya dabarun tsaron yankin Sahel bayan rasa sojojinta a Mali
2019-11-29 11:21:35        cri
Shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron ya ce kasarsa za ta sake yin nazari game da dabarun aikin wanzar da zaman lafiyar da sojojin Faransan ke gudanarwa a yankin Sahel na yammacin Afrika bayan da kasar ta yi hasarar sojojinta 13 a farkon wannan mako a Mali, wannan shi ne hasarar sojoji mafi girma da kasar ta tafka tun lokacin yakin Lebanon a shekarun 1980.

Macron ya fadawa 'yan jaridu bayan tattaunawa da babban sakataren kungiyar tsaro ta NATO Jens Stoltenberg, cewar kasar Faransa tana gudanar da ayyukan tsaro a yankin Sahel a madadin kowa da kowa. Aikin dakarun tsaron Faransa yana da muhimmanci. Sai dai ya ce, halin da ake ciki a yanzu tilas ne su sake yin nazari game da wasu sabbin dabarun da za su yi amfani da su a shirin wanzar da tsaron.

Ya ce, a wannan yanayin da ake ciki, batun shigar da dakarun kawance wajen aikin tabbatar da tsaron yankin Sahel abu ne mai matukar muhimmanci ga kasar Faransa.

Shugaban na Faransa ya bukaci samun kyakkyawan hadin gwiwa da dakarun tsaron nahiyar Turai.

Macron ya ce manufar kasar Faransa game da tabbatar da zaman lafiyar yankin Sahel hakkin tabbatar da tsaro ne na hadin gwiwa wanda take son cimmawa gami da tabbatar da tsaron dakarun kawancenta, domin sauke nauyin dake bisa wuyanta ta hanyar ayyukan soji.(Ahmad Fagam)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China