Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Kasar Sin ta yi kira da ga 'yan kasar Mali su shiga a dama da su a babban taron kasar
2019-10-09 09:34:10        cri
Mataimakin zaunannen wakilin kasar Sin a MDD Wu Haitao, ya yi kira ga dukkan bangarori na kasar Mali, su shiga a dama da su a babban taron tattauna batutuwan kasar, domin wanzar da zaman lafiya da cimma sulhu.

Wu Haitao, ya shaidawa kwamitin sulhu na Majalisar cewa, ya kamata dukkan bangarorin kasar Mali su yi amfani da damar da babban taron ya samar, su hada hannu don samun zaman lafiya da ci gaba a kasar, tare da warware sabanin dake tsakaninsu ta hanyar tattaunawa.

Ya kara da cewa, ya kamata kasashen duniya su bada gudunmuwa mai ma'ana ga kasar Mali, tare da taimakawa wajen karfafa tsarin shugabanci da na ci gaban kasar.

Har ila yau, wakilin na kasar Sin ya ce, kamata ya yi takunkumin kwamitin sulhu a kasar, ya tabbatar da kiyaye manufofin da kwamitin ya gabatar, tare da taimakawa wajen kyautata tsarin siyasar kasar.

Ya kuma yi kira ga kasashen duniya su taimaka wajen bunkasa harkokin tsaron kasar ta yadda gwamnati za ta iya daukar nauyin tabbatar da tsaron kasar da kanta. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China