Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Shugaba Xi ya aike da wasikar taya murnan bude taron kasa da kasa na hadin gwiwar harkokin shari'a
2019-11-10 15:38:26        cri
Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya aike da wasikar taya murnan bude taron kasa da kasa game da hadin gwiwar harkokin shari'a, wanda aka bude a birnin Guangzhou dake kudancin kasar Sin a Lahadin nan.

A cikin wasikar ta sa, shugaba Xi ya ce, gina matakan aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya da Sin ta gabatar, na bukatar tabbaci ta fannin shari'a. Ya ce Sin a shirya take ta yi aiki da sauran kasashen duniya, wajen samar da managartan tsare tsaren shari'a, da kafa sahihan ka'idojin raya tattalin arziki da cinikayya bisa doron doka, masu dacewa kuma a bude.

Kaza lika Sin za ta nace ga aiwatar da matakan bunkasa ci gaban shawarar ziri daya da hanya daya, domin tabbatar da cin gajiya ga daukacin al'ummun kasashe daban daban.

Daga nan sai shugaba Xi ya bayyana fatan cewa, mahalarta taron zai su karfafa musayar ra'ayoyi, da cimma ra'ayi guda, wajen habaka tsarin shari'a, ta yadda hakan zai taimaka ga raya shawarar ziri daya da hanya daya.

Kungiyar ma'aikatan fannin shari'a ta kasar Sin ce dai ta dauki nauyin shirya taron, wanda ya samu mahalarta kusan 400 daga cikin kasar Sin, da kuma kasashen dake cikin shawarar ziri daya da hanya daya 40, tare da wasu kungiyoyin kasa da kasa 4. (Saminu)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China