Facebook Twitter
in Web hausa.cri.cn
Nigeria ta fitar da gargadi game da aukuwar ambaliya a wasu jihohin kudancin kasar
2019-11-05 11:02:59        cri
Hukumar kula da albarkatun ruwa ta Nijeriya, ta fitar da gargadi game da aukuwar ambaliyar ruwa a jiya Litinin ga jihohi 5 na yankin kudancin kasar, tana mai cewa akwai yiwuwar aukuwar ambaliyar ruwa a yankin nan bada dadewa ba.

Hukumar wadda ke da alhakin yin gargadi game da ambaliyar ruwa, ta fitar gargadi na matakin karshe ga jihohin da suka hada da Edo da Delta da Anambra da Rivers da kuma Bayelsa.

Darakta Janar na hukumar Clement Onyeaso Nze, ya bukaci hukumomi a jihohin 5, su lalubo al'ummomin dake iyaka da kogin Niger tare da gudanar da shirye-shiryen ko ta kwana. (Fa'iza Mustapha)

 

Labarai masu Nasaba

 

 

 

 

Mafiya Karbuwa

 

 

 

 

® China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China